Posts

Buhari ya naɗa Manjo Janar Farouk Yahaya a matsayin sabon babban hafsan sojin ƙasan Nigeria

Image
Buhari ya naɗa Manjo Janar Farouk Yahaya a matsayin sabon babban hafsan sojin ƙasan Najeriya. Rundunar sojin ƙasar ce ta sanar da hakan a shafinta na Tuwita a yau Alhamis. Naɗin na zuwa ne kwana shida bayan rasuwar Janar Ibrahim Attahiru mai jagorantar rundunar. Janar Attahiru ya rasu ne a wani hatsarin jirgin sama da ya rutsa da shi a Kaduna, da kuma wasu mutum 11 cikin har da janar-janar uku. W ane ne Manjo Janar Farouk  Yahaya? An haifi Manjo Janar Farouk Yahaya a garin Sifawa na karamar hukumar Bodinga da ke jihar Sokoto a arewa maso yammacin Najeriya a shekarar 1966. Ya shiga aikin soja a 1985 a matsayin dan aji na 37 inda ya kammala karatun soji a ranar 22 ga watan Satumba na 1990. Ya samu karin girma a rundunar soji kamar haka: Laftana - ranar 27 ga Satumba 1990 Kyaftin - ranar 27 ga watan Satumba 1994 Manjo - ranar 27 ga watan Satumba 1998. Laftanar Kanar - ranar 27 ga watan Satumba 2003. Kanar - ranar 27 ga watan Satumba 2008 Birgediya Janar - ranar 27 ga watan...

MAJALISAR DATTAWA TA UMARCI JAMB ta dakatar da amfani da NIN wajen rajista

Image
: NIMC Majalisar Dattawan Najeriya ta umarci Ma'aikatar Ilimi da hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu ta Joint Admission and Matriculation Board (JAMB) da su sake duba shirinsu na amfani da lambar ɗan ƙasa ta National Identity Number (NIN). 'Yan majalisar sun ba su umarnin ne a yau Talata domin ƙara wa'adin rajistar jarrabawar ko kuma soke shirin haɗa rajistar da kuma NIN ga ɗalibai har sai an samar da wani tsari cikakke na samun lambar ta ɗan ƙasa. Kazalika, ƙudirin ya ƙunshi umarni ga Ma'aikatar Ilimi da hukumar samar da NIN ta National Identity Management Commission (NIMC) da su samar da wani tsari mai sauƙi da zai bai wa ɗaliban samun lambar ta NIN a makarantunsu. A 'yan kwanakin nan ne JAMB ta mayar da NIN wajibi ga duk ɗalibin da ke son shiga jami'a a ƙasar. Sanata Ifeanyi Ubah daga Jihar Anambra wanda ya gabatar da ƙudirin, ya ce matakin na JAMB "rashin tausayi ne kuma ya yi wuri". Ƙudirin ya bayyana cewa shirin na JAMB y...

YADDA MATASA SUKA KONA OFISHIN YAN SANDA A JAHAR SOKOTO

Image
Rundunar yan sanda a jihar Sokoto ta tabbatar da mutuwar mutum daya tare da konewar wani ofishin yan sanda da wasu motoci biyu a karamar hukumar Kware. Mai magana da yawun rundunar yan sandan ASP Abubakar Sani cikin wata sanarwa ya ce lamarin ya faru ne bayan da wasu gungun mutane suka je chaji ofis din inda suka nemi a saki wasu mutum biyu da ake zargi masu garkuwa ne. Sanusi ya ce tun farko an kama wadanda ake zargin inda ake gudanar da bincike a kansu saboda samunsu da hannu a garkuwa da mutane a yankin. Ya bayyana cewa gungun akasarinsu matasa sun je ofishin yan sandan inda suka rika ihu tare da neman a saki mutanen biyu da ke tsare. Kakakin rundunar ya kara da cewa mataan sun ci karfin jami'an tsaron da ke kula da ofishin inda suka cinna masa wuta har da motar DPO da wasu motocin yan sanda biyu. A cewarsa, matasan sun halaka daya daga cikin mutanen da ake zargi masu garkuwa ne tare da raunata dayan. Kawo yanzu, ba a kama ko mutum daya ba amma ana ci gaba da gudanar...

Za a biya matasa kimanin naira dubu arba'in idan suka amince a yi musu rigakafin korona

Image
Za a biya matasa kimanin naira dubu arba'in idan suka amince a yi musu rigakafin korona                  Copyright: Getty Images Wata jiha a Amurka ta ce za ta bai wa matasa tukwicin dalar Amurka 100 kwatankwacin kimanin naira dubu arba'in idan suka amince aka yi musu allurar rigakafin korona. Jihar West Virginia ta ce tana fatan ba da tukwicin ga yan shekara 16 zuwa 35 domin basu kwarin gwiwar zuwa a yi musu allurar. A cewar gwamnan jihar, Jim Justice, matasa suna da rawar takawa a yaƙi da annobar ta korona. Jihar tana daga cikin jihohin Amurka da aka tsara yi wa jama'a da yawa allurar rigakafin sai dai lamarin ya fuskanci tsaiko a baya-bayan nan. Akwai fargabar cewa matasa na iya nuna rashin damuwa da zuwa yin rigakafin. Ba da kudin na nufin mutanen da aka yi wa allurar da ke cikin rukunin za su iya samun dalar Amurka 100 da riba a wani lokaci nan gaba. Za kuma a bai wa duk wanda shekarunsa suka kai 16 zuwa 35 da tuni aka yi mus...

An kama mutumin da ya shafa wa mutum 22 cutar korona

Image
An kama wani mutum a Spain da ake zargi da cin zarafi bayan ya yaɗa wa mutum 22 cutar korona. Mutumin mai shekara 40 an yi zargin cewa ya ci gaba da zuwa wurin aikinsa da kuma motsa jiki duk da yana tari kuma zafin jikinsa ya kai sama da 40C. An bayyana cewa yana yawonsa a wurin da yake aiki a Majorca, yana cire takunkumi idan zai yi tari tare da faɗa wa abokan aikinsa cewa zai shafa masu korona. Abokan aikin biyar da wasu mutum uku a wurin da yake zuwa motsa jiki sun kamu da cutar. Wasu mutum 14 cikin ƴan uwansa sun kamu da cutar ciki har da ɗan shekara ɗaya. Ƴan sandan Spain cikin wata sanarwa sun ce mutumin ya daɗe da nuna alamun cutar, amma ya ƙi killace kansa a gidansa da ke Manacor. An yi masa gwaji, amma ya ci gaba da wurin aiki da motsa jiki yayin da yake jiran sakamako ya fito. Ƴan sandan sun ce ya bijerewa abokan aikinsa da ke faɗa masa ya tafi gida. Yana cire takunkumin fuska sai ya yi tari ya fada masu cewa “zan shafa maku cutar korona.”

YADDA AKE DAUKAR SABON FILM DIN ACTOR PRABHAS MAI SUNA SALLER ZA'AFIDDASHI (APRIL 2022)

Image

Allah Ya yi wa Maryam Bayero mahaifiyar Sarkin Kano rasuwa

Image
Allah Ya yi wa Hajiya Maryam Ado Bayero matar tsohon sarkin Kano marigayi Ado Bayero. Mai Babban Daki mahaifiya ce ga Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da Sarkin Bichi Alhaji Nasiru Ado Bayero. Majiyoyin masarautar Kano da suka tabbatar wa BBC da labarin rasuwarta, sun ce ta rasu ne a ranar Asabar a ƙasar Masar. Majiyoyin sun ce ta rasu ne misalin ƙarfe tara na safiyar Asabar. Kuma zuwa gobe ake sa ran yin jana'izarta bayan iso da gawarta zuwa Najeriya daga Masar Babu wata sanarwa kawo yanzu da ta fito daga Masarautar Kano ko gwamnatin Kano game da labarin rasuwar Hajiya Maryam Ado Bayero.